Hotuna: Tagawar Ƙasashe renin Ingila (Kwamanwal) a INEC
A ranar Larabar da ta shige ne Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, da jagororin hukumar su ka karbi baƙuncin wasu maziyarta daga ƙungiyar ƙasashe renin Ingila, wato Kwamanwal masu duba shirye-shiryen gudanar da zaɓe.
Tawagar maziyartan sun zo ne a ƙarƙashin jagorancin Mashawarciya kuma Shugabar Sashen Afrika na ƙungiyar, Ms Abiola Summonu, domin su tattauna kan shirin da hukumar ta yi zuwa yanzu kan Babban Zaɓen shekarar 2023 da za a yi a Nijeriya.
A nan, hotunan da aka yi ne a lokacin ziyarar.
Farfesa Mahmood Yakubu ya na miƙa jakar bayanai ga Madam Abiola Summonu
Farfesa Yakubu ya na gabatar da jawabi ga maziyartan nasa
Wani sashe na maziyartan daga Commonwealth
Post a Comment