An kawo Shaikh Abduljabbar kotu
Tun da sanyin safiyar yau ne, jami'an tsaro suka tare dukkan hanyoyin zuwa babbar kotun musulunci ta jihar Kano inda za a yanke hukunci a shari'ar da gwamnatin Kano ta gurfanar da Sheikh Abduljabar Nasiru Kabara game da zarge-zargen batanci da ake yi masa. Mai Shari'a Alkali Ibrahim Sarki Yola ne zai yanke hukuncin.
Sheikh Abduljabar Nasiru Kabara ya isa kotu Shari'a wacce Sarki Yola ke wa alkalanci, inda za a yanke masa hukunci a shari’ar da gwamnatin Kano ta gurfanar da shi kan zargin batanci da ake yi masa.
Post a Comment