Header Ads

Hauhawar farashin man fetur: Ba wanda ya kara farashin mai a Nijeriya - NNPC

In za a iya tunawa, a baya  kungiyar masu gidajen mai masu zaman kansu reshen jihar  Kano sun shaidawa BBC cewa gwamnatin Nijeriya ta kara farashin man fetur a hukumance da kashi 8.8 inda  a yanzu haka ya ke  185 wasu  wuraren kuma 220 a sassan jihar Legas.

To sai dai kuma a yau Talata  31 ga wannan wata na Janairu shugaban kamfanin na NNPC, Malam Mele Kyari, ya musanta ikirarin kungiyoyin a wurin wani taro na masu ruwa da tsaki a matsalar mai da ake  fama da ita a Nijeriya.

Malam Mele Kyari dai ya nemi mahalarta taron da su bayyana waye  ya kara farashin tare da kawo hujjojinsu na sayen mai a sabon farashin.

Nijeriya dai kasa ce  da Allah ya albarkace ta da man fetur, to sai dai hakan bai hana 'yan kasar fuskantar karancinsa da kuma rashin tabbas wajen farashin ba.

A wajen taron dai an bayyana yanayin jigilar man da kuma rashin daidaito wajen farashin sa a matsayin wasu  daga cikin matsalolin man a Nijeriya.

No comments

Powered by Blogger.