Header Ads

Aminu ya shaki iskar 'yanci


A daren jiya Juma'a ne aka sako É—alibin Jami'ar Tarayya ta Dutse, Aminu Adamu Muhammad daga kurkukun garin Suleja, wurin da wata babbar kotu ta aika da shi bisa tuhumar yin kalaman cin mutuncin matar shugaban Najeriya Aisha Buhari.

Kama wannan dalibin dai ya ja hankulan 'yan Najeriya, har ta kai ga wasu na sukar matakin da hukumomi suka ɗauka, inda a ɗaya ɓangaren kuma wasu ke kallon halin da ya shiga a matsayin izina ga matasan ƙasar masu yawan wallafa sakonni irin wannan a shafukan sada zumunta.

No comments

Powered by Blogger.